October 18, 2025

IAEA Ta Janye Jami’anta Daga Iran Sakamakon Tsanantar Rikici

Flag_of_Iran_(official).svg

Daga Sabiu Abdullahi

Hukumar Kula da Nukiliya ta Duniya (IAEA) ta bayyana cewa ta janye jami’anta daga cibiyoyin nukiliyar Iran, sakamakon tsanantar rikici da ake fuskanta a ƙasar.

Rahotanni sun ce jami’an IAEA ba su sake samun damar shiga cibiyoyin domin sanya ido tun bayan hare-haren da Isra’ila da Amurka suka kai wa cibiyoyin nukiliyar Iran a watan da ya gabata.

Shugaban hukumar, Rafael Grossi, ya bayyana cewa, “sanya idanu kan cibiyoyin nukiliyar Iran shi ne babban muradin hukumar a ƙasar.”

Majalisar dokokin Iran ta kada ƙuri’ar dakatar da hulɗa da IAEA, sai dai ministan harkokin wajen Iran ya bayyana cewa za a ci gaba da wasu ayyukan haɗin gwiwa da hukumar.

Sai dai hukumar IAEA ta ce har yanzu Iran ba ta sanar da ita a hukumance ba game da matakin dakatar da hulɗar.