October 18, 2025

Za mu riƙa biyan N70,000 a matsayin mafi ƙarancin albashi a Edo—Obaseki

IMG-20240430-WA0005.jpg

Daga Sodiqat Aisha Umar

Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki ya sanar da N70,000 a matsayin mafi ƙarancin albashin da za a riƙa biyan ma’aikata a jihar.

Ya sanar da haka ne a wurin kaddamar da sabon ofishin kwadago a jihar Edo.

Gwamnan ya ce sabon mafi ƙarancin albashin zai fara aiki ne daga ranar 1 ga watan Mayu, 2024.

Wannan na zuwa ne yayin da ƙungiyar kwadago ta ƙasa ke ta fafutukar ganin gwamnatin tarayya ta ƙara mafi ƙarancin albashi saboda tsadar rayuwa.