January 14, 2025

Yau jirgin Tinubu zai tashi zuwa Chadi don rantsar da sabon shugaban ƙasa

0
IMG-20240523-WA0004.jpg

Daga Sodiqat Aisha Umar

Shugaban Bola Tinubu zai yi tafiya zuwa ƙasar Chadi a yau Alhamis nufin shaida bikin rantsar da Mahamat Déby a matsayin shugaban ƙasar.

Idan ba a manta ba, farkon wannan watan nan na Mayu ne aka ayyana Mahamat a matsayin wanda ya lashe zaɓen shugaban ƙasar da aka gudanar ranar 6 ga wata Mayu.

Wannan ne karo na farko da Tinubu zai tafi Chadi tun bayan zama shugaban ƙasa a watan Mayun 2023.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *