January 14, 2025

Yanayin tsaro ya sa Gwamnan Benue neman ƙarin jami’an tsaro a jihar

0
Nigerianbandits-750x375-1.png

Daga Sabiu Abdullahi

Gwamna Hyacinth Alia na Benue ya yi kira da a tura karin sojoji da karin sansanonin tsaro a wasu sassan jihar Benue domin magance matsalolin tsaro da suka addabi jihar.

Mista Alia ya yi wannan kiran ne a lokacin da ya kai ziyarar ban girma ga babban hafsan sojin kasar, COAS, Laftanar-Janar Taoreed Lagbaja, ranar Talata a Abuja.

Ya bukaci a kafa sansanonin gudanar da ayyukan tsaro a kananan hukumomin Guma, Logo, Ukum da Kwande don taimakawa wajen dakile matsalar tsaro a yankunan. 

Ya ce mutanen Benue manoma ne sannan galibin yankunan da za a iya nomawa a Benue sun zama ba sa zaunuwa ga manoma saboda barazanar ‘yan fashi da tashin hankali daga makiyaya.

A cewarsa, ana kashe mutane biyu zuwa biyar ko fiye a kowane mako sakamakon tashin hankalin da wadannan kungiyoyi ke yi, wanda a wasu lokuta ‘yan jaridu ba sa bayyanawa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *