January 15, 2025

Yajin aiki ya sa an rufe ƙofofin zauren majalisun Najeriya

0
images-2023-11-14T134707.926.jpeg

Daga Sabiu Abdullahi

Ginin majalisu a Najeriya da ke Abuja suna rufe yayin ƙungiyoyin ƙwadago suka shiga yajin aiki

Idan dai za a iya tunawa, kungiyar Kwadago ta Najeriya da kungiyar ‘yan kasuwa sun sanar da fara yajin aikin sai baba-ta-gani a faɗin kasar daga yau Talata duk da umarnin da kotu ta bayar na hana kungiyoyin yin hakan.

Rahotannin sun nuna cewa a makon da ya gabata kungiyar ƙwadagon ta fitar da sanarwar yajin aikin a faɗin kasar sakamakon wani hari da aka kai wa Joe Ajaero, shugaban kungiyar NLC, a ranar 1 ga Nuwamba, 2023, a jihar Imo.

Da misalin karfe 12:23 na daren ranar Talata lokacin da ƴan jarida suka ziyarci harabar majalisar, dukkanin kofofin da kai ga zuwa harabar majalisar na kulle da makulli.

An ga ma’aikata da dama sun maƙale a ƙofar shiga majalisar, sai dai wakilinmu ya ruwaito cewa, duk da kulle-kullen da aka yi, zaman majalisar na ci gaba da gudana a zauren majalisar har ya zuwa lokacin da wannan rahoto ya fito.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *