January 15, 2025

Wata cibiya a Saudiyya ta ɗauki nauyin raba wasu tagwayen da suka manne a Kano

0
IMG_3224.jpeg

Daga Sabiu Abdullahi

Cibiyar Bayar da Agaji ta Sarki Salman (KSARelief) da ke kasar Saudiyya ta bayyana shirin gudanar da aikin tiyatar raba wasu tagwaye Hassana da Husaina Hassan Isa daga Kano, Najeriya.

Muhammad Alsahabi, mai magana da yawun ofishin jakadancin Saudiyya a Abuja ne ya sanar da hakan.

Hassana da Husaina, wadanda suka haɗe a kirji da kuma wasu muhimman gaɓoɓin jiki, suna fuskantar wasy matakan masu sarƙaƙiya a wajen raba su.

Labarin nasu ya ɗauki hankalin miliyoyin mutane a duk duniya.

Yana kuma nuna buƙatar gaggawa don samun kulawar likita ta musamman ga irin waɗannan matsalolin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *