December 7, 2025

Uwargidan Tinubu ta ba wa ɗalibai marasa galihu tallafi a Nasarawa

FB_IMG_1727081327549

Uwargidan Shugaba kasa, Sanata Oluremi Tinubu, ta rarraba wa ɗalibai marasa galihu littafan rubutu a Jihar Nasarawa.

Remi Tinubu wadda ta bayyana samar da nagartaccen ilimi a matakin farko a matsayin tubalin ci gaban ƙasa.

Ta yi rabon littafan rubutun ne guda 60,000 ga ɗalibai marasa galihu a faɗin ƙananan hukumomi 13 na Jihar Nasawara.

Da take ƙaddamar da rabon littafan, uwargidan shugaban ƙasar, wadda matar Gwamnan jihar Nasarawa, ta wakilta, ta ce ilimi a matakin farko wani bigire ne da ke da muhimmanci wajen bunƙasar kasar nan.

Remi Tinubu ta jaddada ƙudirin Gwamnatin kasar nan, a dukkan matakai wajen bunƙasa harkokin ilimi ta fuskar inganci da kuma sauƙi musamman a tsakanin waɗanda ke da rauni a cikin al’umma.