January 15, 2025

Tsohon gwamnan Kaduna Ramalan Yero ya koma jami’iyyar APC

0
images-157.jpeg

Daga Abdullahi I. Adam

Tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Alh. Mukhtar Ramalan Yero ya bayyana cewa ya amince ya koma jam’iyyar APC.

Idan ba a manta ba, tsohon Gwamnan ya sanar da ficewa PDP ne a watannin baya duk da cewa ita ce jam’iyyar da ya riƙe manyan muƙamai ƙarƙashinta inda ya zamo kwamishina, mataimakin gwamna har zuwa matakin gwamna.

A faifan bidiyon da wani makusancinsa ya saki a kafar sadarwa ta Facebook, an jiyo tsohon gwamnan na faɗar cewa ya yanke wannan shawara e bayan ya tuntuɓi makusantansa a siyasance.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *