January 24, 2025

Tinubu ya rantsar da Kekere-Ekun a matsayin sabuwar Alƙaliyar Alƙalai

0
ei_1724430700496-removebg-preview

Daga Sabiu Abdullahi

A yau ne Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu ya rantsar da Mai Shari’a Kudirat Kekere-Ekun a matsayin sabuwar Alƙaliyar Alƙalan ƙasar ta riƙo, kafin Majalisar Dattawan ƙasar ta tabbatar da naɗin nata.

An naɗa ta a kan muƙamin ne bayan Alƙalin Alƙalan ƙasar Olukayode Ariwoola ya yi ritaya a jiya Alhamis.

Wace ce Kudirat?

An haifi Kudirat Motonmori Olatokunbo (CFR) a ranar 7 ga watan Mayun 1958 a birnin London da ke ƙasar Birtaniya.

Sannan an fi saninta da Kudirat Kekere-Ekun.

Ƙwararriyar lauya ce a Najeriya kuma mai shari’a ta Kotun Koli ta Najeriya.

A shekarar 1980, ta kammala digirinta na farko a fannin shari’a daga Jami’ar Legas, kuma ta samu gurbin karatu a Nigerian Bar a ranar 10 ga Yuli 1981, bayan ta kammala makarantar koyon aikin lauya ta Najeriya.

Daga bisani ta wuce Makarantar Tattalin Arziki ta London inda ta samu digiri na biyu a fannin shari’a a watan Nuwamba 1983.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *