February 10, 2025

Shugaba Tinubu Zai Ziyarci Faransa Kafin Halartar Taron AU a Habasha

2
FB_IMG_1738752352416.jpg

Shugaba Bola Ahmed Tinubu zai bar Abuja a ranar Laraba don wata ziyarar zuwa birnin Paris na ƙasar Faransa, kafin ya wuce zuwa Addis Ababa, babban birnin Habasha.

A Addis Ababa, Shugaba Tinubu zai halarci taron shugabannin Afirka a zama na 46 na majalisar zartarwa da kuma zama na 38 na shugabannin ƙasashen kungiyar Tarayyar Afirka (AU), wanda zai gudana daga ranar 12 zuwa 16 ga watan Fabrairu, 2025.

Ana sa ran shugaba Tinubu zai isa Addis Ababa a farkon mako mai zuwa domin halartar taron koli na Tarayyar Afirka.

A yayin ziyararsa a Faransa, Shugaba Tinubu zai gana da takwaransa na ƙasar, Shugaba Emmanuel Macron.

2 thoughts on “Shugaba Tinubu Zai Ziyarci Faransa Kafin Halartar Taron AU a Habasha

  1. Hi there i am kavin, its myy first time to ommenting
    anywhere, when i rerad this piece of writing i thought i could
    aso create comment duue too this brilliant article.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *