January 15, 2025

Shugaba Tinubu ya miƙa wa Gwamnan Akwa Ibom ta’aziyya bisa rasuwar uwargidansa 

0

Daga Sabiu Abdullahi  

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya mika sakon ta’aziyyarsa ga gwamnan jihar Akwa Ibom, Fasto Umo Eno, bayan rasuwar mai dakinsa Fasto Patience Umo Eno.  

A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Bayo Onanuga ya fitar, Shugaba Tinubu ya jajanta wa iyalan Eno, gwamnati, da al’ummar jihar Akwa Ibom a wannan lokaci na baƙin ciki.

Tinubu ya yabawa uwargidan gwamnan, inda ya nuna goyon bayanta ga gwamnatin Gwamna Eno.  

“Patience Eno, a matsayin matar gwamna mai hangen nesa kuma mai hidimar bushara, tana da tawali’u, juriya, da aminci,” in ji shi.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *