Sarkin Musulmi ya ce a fara duba watan Ramadan daga gobe Lahadi
Daga Sabiu Abdullahi
Mai alfarma Sarkin Musulmi, Alhaji Sa’ad Muhammad Abubakar ya yi kira ga al’ummar Musulmi a Najeriya da su fara duban watan Ramadan daga gobe Lahadi.
Wannan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da Salisu Shehu, sakataren majalisar koli ta addinin Muslunci ta ƙasa ya fitar a yau Asabar.
A cewarsa, za a fara azumin Ramadan kai tsaye ranar Talata matukar ba a ga watan ba a ranar Lahadi.