January 14, 2025

Rashin lantarki ya sa gawarwaki na ta ruɓewa a ɗakunan ajiya gawa na barikin soja—Lagbaja

0
images-197.jpeg

Daga Sabiu Abdullahi

Rashin wutar lantarki a barikin sojojin Najeriya ya haifar da ruɓewar gawarwakin da ke dakin ajiyar gawarwaki.

Babban hafsan sojin kasa Najeriya, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja, ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a yayin da yake neman sa hannun ministan wutar lantarki, Adebayo Adelabu.

Ya kuma yi kira da a biya bashin wutar lantarkin da ake bin sojojin Najeriyar na naira biliyan 42.

Wannan bukata ta zo ne bayan da kamfanonin samar da wutar lantarki suka yanke wutar barikin Sojoji da dama.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *