February 10, 2025

Ranar Talata babu aiki a Najeriya saboda bikin samun ƴancin kai na 1 ga Oktoba

1
images (13) (26)

Daga Sodiqat A’isha Umar

Gwamnatin Tarayya ta ayyana Talata, 1 ga watan Oktoba a matsayin ranar hutu cikar Nijeriya shekara 64 da samun ’yancin kai.

Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo, ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa da Babbar Sakatariyar Ma’aikatar, Dokta Magdalene Ajani, ta fitar a ranar Asabar din nan.

Ministan ya ce duk tarin kalubalen da kasar nan ke fuskanta, gwamnati na iya bakin kokarinta wajen ganin ta magance su.

Ministan ya kuma taya dukkan ’yan kasar na gida da na ketare murnar zagayowar ranar da kasar nan ta samun yacin kanta daga turwar mulki mallaka.

1 thought on “Ranar Talata babu aiki a Najeriya saboda bikin samun ƴancin kai na 1 ga Oktoba

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *