January 15, 2025

Netanyahu ya sha alwashin ci gaba da kisar gilla a Gaza

1
17_47_48_images

Daga Sabiu Abdullahi

Firaministan Isra’ila, Benjamin Netanyahu, ya bayyana cewa yakin da kasarsa ke yi a Gaza, wanda ya kai shekara guda, zai ci gaba da gudana muddin kasarsa tana fuskantar barazana.

Ya bayyana cewa ba zai yiwu a dakatar da hare-haren da Isra’ila ke kaiwa Gaza, Lebanon, da wasu yankunan Gabas ta Tsakiya ba, domin suna fafatawa da abokan gaba.

“Wannan nauyi ne da ya rataya a wuyanmu, ba za mu dakata ba sai mun kammala aikin da ya wajaba a kanmu,” in ji Netanyahu yayin jawabin da ya gabatar ga ‘yan kasar bayan zagayowar ranar 7 ga Oktoba, lokacin da Hamas ta kai harin ramuwa kan Isra’ila.

A lokaci guda, Isra’ila ta ci gaba da kai hare-hare a birnin Beirut na Lebanon, yayin da kungiyar Hezbollah ta harba rokoki sama da 100 zuwa Isra’ila a jiya, Litinin.

1 thought on “Netanyahu ya sha alwashin ci gaba da kisar gilla a Gaza

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *