February 10, 2025

Manchester City Za Ta Gwabza da Real Madrid a Champions League

2
image_editor_output_image-64827496-1738332599843.jpg


Hukumar kula da kwallon kafa ta Turai ta fitar da jadawalin wasannin matakin sili ɗaya kwale na gasar Champions League, wanda zai bai wa kungiyoyin da suka yi nasara damar kaiwa zagaye na gaba.

Daya daga cikin wasannin da ake sa ran zai ja hankali shi ne tsakanin Manchester City da Real Madrid. Man City, wadda ta lashe kofin a 2023, za ta karɓi baƙuncin Madrid a filin Etihad a ranar 11 ko 12 ga watan Fabrairu, yayin da wasan na biyu zai gudana a Sifaniya bayan mako guda.

A wasu wasannin kuma, Celtic za ta kara da Bayern Munich, inda za a fara wasa a Scotland kafin su tafi Jamus.

Jadawalin Wasannin Zagaye na Biyu

Feyenoord da AC Milan

Sporting da Borussia Dortmund

Club Brugge da Atalanta

Celtic da Bayern Munich

Juventus da PSV Eindhoven

Monaco da Benfica

Brest da Paris St-Germain

Manchester City da Real Madrid


Za a fafata wasannin zagaye na biyu a cikin watan Fabrairu da Maris, inda kowace kungiya za ta yi iya bakin kokarinta don cimma nasara.

2 thoughts on “Manchester City Za Ta Gwabza da Real Madrid a Champions League

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *