December 7, 2025

Majalisa za ta binciki yadda manyan makarantun Najeriya ke ba da gurbin karatu bisa ka’ida ba

IMG-20231109-WA0003.jpg

Daga Usama Taheer Maheer

Majalisar dattijai za ta yi bincike akan yadda makarantun gaba da sakandare ke bayar da gurbin karatu ba bisa ka’ida ba.

Majalisar Dattijai ta umarci kwamitinta na ɓangaren makarantun gaba da sakandare da kwamitin karɓar ƙorafe-ƙorafen al’umma, da su yi binciken a kan zargin da ake yi wa makarantun gaba da sakandare a kan bayar da da gurbin karatu ga waɗanda ba su cancanta ba.
Ana sa ran kwamitocin za su sanya hukumar JAMB a cikin binciken nasu.

Ana sa ran kwamitocin za su sanya hukumar JAMB a cikin binciken nasu.

Da yawan ƙorafe-ƙorafe na nuna cewa, jami’o’i da kwalejoji suna haɗa baki da hukumar JAMB wajen ba wa waɗanda basu cacanta ba gurbin karatu.

Tun da fari, ɗan majalisar da ke wakiltar Ebonyi ta arewa, Mista Nwebonyi Onyeka, shi ya karanta ƙudirin a gaban majalisar. Yayin da ya samu goyon bayan ƴan majlissu da dama.

Yayin Jawabin ɗan majalisar, ya yi zargin cewa, ana samun haɗin gwiwa da hukumomin makarantun gaba da sakandare da hukumar JAMB wajen samar wa da ɗalibai gurbin karatu ba bisa ƙa’ida ba.

Ɗan majalisar ya ƙara da cewa, yawanci ana karɓar kuɗin ɗaliban da ke neman kwasa-kwasan da ke da wahalar samu, kamar karatun likitanci, karatun sarrafa magunguna, karatun shari’a, da karatun injiniyarin har ma da karatun masu jinya a sibiti.

Ya kuma yi zargin cewa, da yawan ɗaliban da suke da hazaƙa, sun shiga damuwa, wasu ma sha’awar karatun ya fita daga ransu saboda wannan rashin adalcin.

14 thoughts on “Majalisa za ta binciki yadda manyan makarantun Najeriya ke ba da gurbin karatu bisa ka’ida ba

  1. Great beat ! I would like to apprentice while you
    amend your site, how could i subscribe for a blog site? The account
    aided me a acceptable deal. I had been tiny bit acquainted of this
    your broadcast offered bright clear idea

  2. Your style is unique compared to other folks
    I have read stuff from. I appreciate you for posting when you
    have the opportunity, Guess I will just book mark this web site.

  3. Hi would you mind letting me know which hosting company you’re using?
    I’ve loaded your blog in 3 completely different browsers and
    I must say this blog loads a lot faster then most.
    Can you suggest a good hosting provider at a honest price?

    Cheers, I appreciate it!

  4. I’m curious to find out what blog system you are utilizing?
    I’m having some small security issues with my latest blog and I would
    like to find something more risk-free. Do you have any solutions?

Comments are closed.