January 24, 2025

Magoya Bayan Guinea Guda 6 Sun Rasa Rayukansu Yayin Murnar Samun Nasara

0
image_editor_output_image-345370964-1706012736435.jpg

Daga Sabiu Abdullahi

Magoya bayan tawogar ƙwallon ƙafar Guinea guda shida ne suka mutu a lokacin da suke kina farin cikin samun nasara a wasan farko da suka samu a gasar cin kofin Afrika.

Feiguifoot, wadda ita ce hukumar kwallon kafa ta Guinea, ita ta tabbatar da faruwar lamarin a jiya Litinin.

Ta ce lamarin ya faru ne a yayin bikin murnar da aka yi a titunan Conakry, babban birnin kasar.

Idan mai karatu bai manta ba a halin yanzu ana ta gudanar da gasar cin kofin Afrika a Ivory Coast.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *