January 14, 2025

Limamai a Saudiyya ba za su yi dogayen huɗubobi a salloli gobe ba don zafin rana

1
IMG-20240606-WA0034.jpg

Daga Abdullahi I. Adam

Babban limamin Harami, Asshaikh Abdurrahman Al-Sudais, ya ba da sanarwar cewa limamai su gajarta huɗubobi da sallolin da za a gabatar a gobe Juma’a.

Kamar yadda babban limamin ya ambata, wannan umurni ya biyo bayan tsananin zafin rana da ake fama da shi ne a ƙasar wadda a yanzu haka take cike maƙil da maniyyata.

Sanarwar wadda aka wallafa a shafin Facebook na “Inside the Haramain” na zuwa ne daidai lokacin da hukumomi a ƙasar ke cigaba da samar da hanyoyin kula da mahajjata waɗanda wasunsu ba za su iya jure ma irin zafin rana da ake yi a ƙasar ba.

1 thought on “Limamai a Saudiyya ba za su yi dogayen huɗubobi a salloli gobe ba don zafin rana

  1. Hey there this iis kinda of off topic but I was wondering
    if blogs use WYSIWYG editors or if you have to
    manually code with HTML. I’m starting a blog soon bbut have no coding skills so I wanted to get advice from someone with experience.

    Any help would be greatly appreciated! https://ukrain-Forum.biz.ua/

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *