December 7, 2025

Gwamnatin Najeriya ta ƙaddamar da shirin gyaran hanyoyin ƙasar

14_57_34_images

Daga Sabiu Abdullahi

Mataimakin shugaban ƙasa Kashim Shettima ya bada umarnin ƙaddamar da yin garambawul ga hanyoyin kasar nan.

Umarnin na da nufin magance kalubalen hanyoyi da inganta hanyoyin da rage haddura dake faruwa a fadin ƙasar nan, musamman a lokacin damina.

Shettima, ya ba da wannan umarnin ne yayin ganawa da shugaban hukumar kula da ingancin hanya ƙarƙashin jagorancin Shehu Mohammed, wanda ya gudana a fadar shugaban ƙasa da ke babban birnin tarayya Abuja.

Hadimin mataimakin shugaban ƙasa a kafafan yada labarai, Stanley Nkwocha, ne ya sanar da haka cikin wata sanarwa a jiya Juma’a.

A cewarsa, mataimakin shugaban ya shirya ƙaddamar da majalisar bada shawara ta kan kula da lafiyar hanyoyi, wacce za ta dauƙi alhakin yawaitar rage cunkoson ababen hawa nan da shekarar 2030.

Shettima ya jaddada bukatar rage yawaitar haɗɗura a manyan hanyoyi da birane.