January 24, 2025

Gwamnatin Kano za ta rushe katangar gidan Sarki da ke Nasarawa

0
IMG-20240606-WA0026.jpg

Daga Sabiu Abdullahi

Gwamnatin jihar Kano za ta fara aikin rushe katangar gidan Sarki na Nasarawa da Sarkin Kano na 15 Aminu Ado Bayero ke ciki.

A cewar gwamnatin, za ta yi hakan ne “saboda ya lalace”.

Kwamashinan Shari’a na Kano Haruna Isa ne ya bayyana hakan yayin taron manema labarai da ya gudanar a gidan gwamnati.


Gwamnatin ta kuma ba da umurni wa kwamishinan ‘yansandan jihar da ya fitar da Aminu Ado daga gidan bayan hukuncin kotu a yau Alhamis, wanda ta yi iƙirarin cewa ya ba ta nasara a kan ɓangaren da suka shigar da ƙarar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *