January 15, 2025

Gwamnatin Borno Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Nazarci Rikicin Manoma Da Makiyaya

0
IMG-20240121-WA0007.jpg

Daga Sabiu Abdullahi

Gwamnatin jihar Borno ta kafa kwamitin mutum 10 da zai binciki musabbabin rikici tsakanin manoma da makiyaya a fadin jihar da nufin magance su.

Kwamitin dai zai “sake kafa dusassun hanyoyin kiwon shanu da kuma gano wuraren kiwo da ba a yin amfani da su sosai ba.”

Gwamna Babagana Zulum ya kaddamar da dokokin kwamitin a garin Gamboru da ke kan iyakar Najeriya da Kamaru a ranar Litinin.

Ya ce dokokin kwamitin na daya daga cikin matakan da gwamnatin jihar ke dauka domin dakile rikicin manoma da makiyaya a fadin jihar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *