January 15, 2025

Gwamnan Kano Abba Kabir ya tafi Kotun Ƙoli bayan hukuncin kotun ɗaukaka ƙara

0
Abba-Yusuf.jpg

Daga Sabiu Abdullahi


Gwamnan jihar Kano Abba Yusuf wanda kotun daukaka kara ta tabbatar da tsige shi, ya bayyana aniyarsa na kalubalantar hukuncin a kotun koli.

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta tabbatar da hukuncin kotun, inda ta kori Yusuf tare da bayyana Nasiru Gawuna na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben ranar 18 ga watan Maris.

A wani jawabi da ya yi ta gidan talbijin a daren Juma’a, Gwamna Yusuf ya tabbatar da aniyarsa ta maido da abin da ya ke ganin hakkinsa ne.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *