February 12, 2025

Dole a rage kuɗin wutar lantarki a Najeriya—NLC

0
IMG-20240502-WA0018.jpg

Daga Sodiqat Aisha Umar

Kungiyar Kwadago ta Najeriya (NLC) ta ba wa gwamnati da kamfaninin wutar lantarki wa’adin mako guda su soke karin kudin da suka yi a kasar nan. 

Shugaban NLC na kasa, Kwamred Joe Ajaero da takwaransa na hadaddiyar kungiyar ma’aikata (TUC) Fetus Osifo ne, suka bada wa’adin a jawabinsu na hadin gwiwa a ranar ma’aikata a jiya laraba a babban birnin tarayya Abuja.

A Don haka suka ce ya zama dole Hukumar Wutar Lantarki (NERC) da kamfanonin wutar su soke karin kudin wutar.

Kungiyoyin sun bayyana takaicinsu bisa rashin samun tsayayyiyar wutar lantarki a kasar nan, inda suka bayyana cewa hakan yana kawo koma-baya ga cigaban tattalin arzikin kasar.

Sun bayyana cewa duk kasar da ta gaza sama wa kanta wadacciyar wutar lantarki da makamashi, babu makawa sai ta samu koma-baya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *