March 28, 2025

Cutar ƙyandar biri ta addabi nahiyar Afirka

IMG-20240809-WA0007

Daga Sodiqat Aisha Umar

Hukumar yaƙi da yaɗuwar cututtuka ta Afirka ta ce nan ba da jimawa ba, za ta ayyana cutar ƙyandar biri da ta ɓarke a nahiyar, a matsayin wata matsala da ke buƙatar kulawar gaggawa.

Daraktan hukumar ya ce ya kaɗu da yadda aka samu ƙaruwar mutanen da ke ɗauke da cutar da kashi 160 cikin 100 a shekarar da ta gabata.

Wani nau’in cutar na yaɗuwa sosai a jamhuriyar Dimokraɗiyyar Kongo inda cutar ta fi ƙamari.

Majalisar Ɗinkin Duniya ta ba da rahoton bazuwar cutar a sassan Afirka a wannan shekarar.

Ƙasashe 16 ciki har da Rwanda da Burundi da Uganda da Kenya duk sun sanar da ɓarkewar cutar.