January 14, 2025

Babban hafsan sojin Najeriya ya yi liyafar salla da sojojin da suke asibiti

0
Eid-el-Kabir-COAS-celebrates-with-wounded-soldiers-in-Kaduna.jpg

Daga Sabiu Abdullahi

Yayin da ‘yan uwa Musulmi ke gudanar da bukukuwan Babbar Sallah a ranar Lahadi, babban hafsan sojin kasa, Laftanar Janar Taoreed Lagbaja, ya yi liyafa tare da wasu sojojin da suka samu raunuka a asibitin sojoji na 44 da ke Kaduna.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya ya rawaito cewa, an raba kayan abinci iri-iri da abubuwan sha ga sojojin a wani bangare na bukukuwan Sallah.

Da yake jawabi a wajen taron, Mista Lagbaja ya ce Idi rana ce ta murna da kyauta wa mabukata. 

Hukumar ta COAS ta ce bikin Eid-el Kabir ya kunshi yin murna tare da sojoji musamman a lokaci guda.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *