January 15, 2025

‘Ba wanda ya isa korata daga jam’iyyar NNPP’

16
images-5-22.jpeg

Daga Sabiu Abdullahi

Tsohon gwamnan Kano, kuma jagoran jam’iyyar NNPP na kasa a Najeriya Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, ya fada cewa har yanzu su ne ainihin ƴa’ ƴaƴan jam’iyyar kuma sun shigeta ne don samar da kyakkyawar manufa ta ceto Najeriya.

Hakan dai na zuwa ne lokacin da yake mayar da martani kan ikirarin korar sa daga jam’iyyar ta NNPP da wasu yan jam’iyyar suka ce sun yi, a kwanakin baya.

A cewarsa, babu wanda ke da ikon korar sa daga jam’iyyar da suka raya har ta kai ga matakin da ta kai a yanzu.

An ambato shi yana cewa, “Mu a ganinmu waɗannan mutane ba yan siyasa bane, basu fahimci yadda tsarin yake ba, ni ba shugaba bane kawai na Kano, nine jagoran wannan jam’iyya a Najeriya baki daya, lallai ana son kowa ya shigo wannan jam’iyya, ba za a ce ba a so wani ya shigo ba, wannan jam’iyya ba ta kowa bace.

“Dimukradiyya na da dadi, kuma tana da wuya, a tsari duk lokacin da aka ce hukuma ko jam’iyya ta yi karfi kamar yadda wannan jam’iyya take kankanuwa kafinm mu shigo ta yi karfi a yanzu, muna da sanatoci da yan majalisar wakilai, da gwamna da Rabiu Musa Kwankwaso da Buba Galadima da sauransu, to ka ga dole abubuwa sun sauya daga yadda suke a baya.”

16 thoughts on “‘Ba wanda ya isa korata daga jam’iyyar NNPP’

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *