Ana zargin sojojin Isra’ila da kama ɗaruruwan Falasɗinawa tare da barinsu cikin yunwa da ƙishirwa

Daga Sabiu Abdullahi
Sojojin Isra’ila sun kakkama daruruwan Falasdinawa a yankin arewacin Zirin Gaza, inda suka raba su da iyalansu tare da tilasta wa maza tube riga kafin su tasa ƙeyarsu zuwa magarkama da ke gabar teku.
A cewar wani rahoto na AP, Falasdinawan da aka kama sun shafe sa’o’i cikin fama da yunwa da sanyi kamar yadda masu rajin kare hakkin bil’adama da ‘yan uwansu da kuma fursunonin da aka sake suka bayyana.
Falasdinawa da ake tsare da su a garin Beit Lahiya da sansanin ‘yan gudun hijira na Jabaliya da kuma unguwannin birnin Gaza sun ce an daure su, tare da rufe musu idanuwa.
Wannan na zuwa ana a daidai lokacin da al’amurra suke kara tsamari da ta’azzara a yaƙin da ake yi tsakanin Hamas da Isra’ila.
Thank you for addressing such an important topic in this post Your words are powerful and have the potential to make a real difference in the world
Thank you for addressing such an important topic in this post Your words are powerful and have the potential to make a real difference in the world
Your posts always speak to me on a personal level and I believe that is a testament to your authenticity and genuine nature
Your writing has a way of making me feel like I’m having a conversation with a close friend It’s so genuine and relatable
This blog is such a hidden gem I stumbled upon it by chance and now I’m completely hooked!