January 14, 2025

An kama wasu suna lalata a cikin coci a Maiduguri

0
idt6v2.jpg

Daga Sabiu Abdullahi

Rundunar ‘yan sandan jihar Borno ta kama wani matashi da wata matashiya da laifin yin lalata a cikin Cocin Protestant da ke Kwalejin ‘yan sanda da ke Maiduguri a jihar Borno.

Mutanen da aka kama ɗin dai su ne Kaka Ali Umar wanda ya fito daga titin Damboa da kuma Khadija Adam mazauni unguwar Ngomari a Maiduguri.

Rahotanni sun nuna cewa lamarin ya faru ne a ranar Litinin.

A cewar Rabaran Danjuma Adamu, limamin cocin, an kama mutane biyun ne a cikin harabar cocin.

Rabaran Adamu ya nuna rashin jin daɗinsa kan yadda aka wulakanta wannan wuri mai tsarki, inda ya bayyana lamarin a matsayin abin kunya da cin amana.

Rabaran ɗin ya ce, “Mun garzaya cikin cocin, sai ga shi mun gamu da Musulmai biyu da ke wannan aika-aika, inda nan take muka sanar da ‘yan sanda.”

Ya bayyana girman al’amarin, inda ya nuna buƙatar a gaggauta ɗaukar mataki domin kare martabar cocin.

An ce dai mutanen biyu ba su musanta zargin ba, kuma sun yarda sun yin lalata a cikin cocin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *