January 15, 2025

Allah Ya yi rasuwa wa tsohon firaministan Nijar Hama Amadou

0
66803294_803.jpeg

Daga Sabiu Abdullahi

Tsohon Firaministan Jamhuriyar Nijar, Hama Amadou, ya rasu a daren Laraba bayan fama da jinya, kamar yadda wasu daga cikin makusantansa suka tabbatar. 

Rahotanni sun bayyana cewa Hama Amadou, wanda ya taba shugabancin majalisar dokokin Nijar, ya rasu ne a kan hanyarsa ta zuwa babban asibitin birnin Yamai.

An haifi marigayi Hama Amadou a ranar 3 ga watan Maris, shekarar 1950, a garin Youri da ke cikin jihar Tillabery, yankin yammacin Nijar, yana da shekaru 74 a lokacin rasuwarsa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *