May 17, 2025

AKWAI RINA A KABA: Kotu ta ayyana zaɓen gwamnam Zamfara a matsayin wanda bai kammala ba

WhatsApp-Image-2023-11-14-at-17.19.21_a22dc76d-e1699983001656.jpg

Daga Sabiu Abdullahi

Kotun daukaka ƙara da ke zamanta a Abuja ta ayyana zaben gwamnan jihar Zamfara a matsayin wanda bai kammala ba.

Idan ba a manta ba, hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa ta ayyana Dauda Lawal na jam’iyyar Peoples Democratic Party  wanda ya lashe zaben.

Ɗan takarar gwamnan jam’iyyar All Progressives, Bello Matawalle, ya ƙalubalanci sakamakon zaɓen gwamnan da za a yi a ranar 18 ga watan Maris a kotun amma an yi watsi da kokensa saboda rashin cancanta.

Da ake yanke hukuncin a ranar Alhamis ne, kotun ɗaukaka ƙara ta bayyana zaben a matsayin wanda bai kammala ba kuma kotun ta umarci INEC da ta gudanar da sabon zaɓe a kananan hukumomi biyu.

1 thought on “AKWAI RINA A KABA: Kotu ta ayyana zaɓen gwamnam Zamfara a matsayin wanda bai kammala ba

  1. Someone necessartily help too maje seriously posts Imioght state.
    Thatt iss tthe very firs time I frequented yojr web page aand to this point?
    I amazed with the anapysis you made tto create this
    actual putt upp amazing. Magnificejt process!

Comments are closed.