February 10, 2025

‘Adadin talakawa a Najeriya ya ƙara ninninkuwa’

0
images-21.jpeg

Bankin duniya ya fitar da rahoton ci gaban Najeriya, inda a ciki ya ce sama da mutum miliyan 129 ne suke zaune cikin talauci a ƙasar.

A rahoton wanda bankin ya fitar jiya Alhamis a Abuja, ya nuna hauhawan farashin kayayyaki ne ye jefa miliyoyin ƴan ƙasar a cikin yunwa, kamar yadda Channels ta ruwaito.

Bankin ya ce sama da mutum miliyan 129, ya nuna ƴan ƙasar masu fama da talauci ya ƙaru ne daga kashi 40.1 a shekarar 2018 zuwa kashi 56 a shekarar 2024.

Rahoton ya ƙara da cewa a shekarar 2023 mutum miliyan 115 ne suke fama da talauci, wanda hakan ke nufin an samu ƙarin mutum miliyan 14 a bana.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *