Ɗan majalisa a Najeriya zai aurar da marayu mata guda 100
Daga Sabiu Abdullahi
Ɗan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Argungu/Augie ta jihar Kebbi a majalisar wakilai ta kasa Sani Yakubu Noma ya bayyana cewa ya kammala shirye-shiryen taimakon marayu mata 100 domin aurar da su.
Da yake zantawa da manema labarai a mahaifarsa da ke yankin Argungu a jihar Kebbi, dan majalisar ya ce shirin auren na ɗaya daga cikin gudunmawar da yake bayarwa wajen kyautata rayuwar marayu a mazabarsa.
Ya ce za a ɗaura auren ne a fadar mai martaba Sarkin Argungu, Alhaji Sama’ila Muhammad Mera ranar Asabar.
“An kafa kwamiti don samun nasarar aiwatar da shirin. Wadanda aka zaba domin a daura musu aure sun fito ne daga kananan hukumomin biyu da nake wakilta a Majalisar Dokoki ta kasa.
“Tuni, na sayi gadaje, katifu, kayan aiki masu mahimmanci da sauran kayayyakin aure ga wadanda suka ci gajiyar,” in ji shi.
капельница от запоя на дому в Коломне капельница от запоя на дому в Коломне .
Лечение наркомании в Казахстане Лечение наркомании в Казахстане .
taif моторное масло официальный сайт https://www.e-taif.ru .
алкоголизм симптомы лечение алкоголизм симптомы лечение .