January 14, 2025

Ɗaliban jami’a a Nasarawa sun shaƙi iskar ƴanci bayan shafe kwanaki a hannun ƴan bindiga

0
images-2023-12-11T094104.544.jpeg

Daga Sabiu Abdullahi

An sako daliban Jami’ar Tarayya ta Lafia (FULAFIA) guda bakwai da aka yi garkuwa da su kwanaki hudu da suka gabata.

An sako daliban ne a yammacin Lahadi bisa kokarin hadin gwiwa na sojoji da sauran jami’an tsaro.

Shugaban Majalisar Wakilan Dalibai Ibrahim Ogbo ya tabbatar da sakin nasu a wata tattaunawa da ƴan jarida.

Daliban, wadanda suka kunshi mata uku da maza hudu, suna asibitin makarantar har zuwa lokacin gabatar da wannan rahoto.

An yi garkuwa da daliban ne a daren ranar Larabar da ta gabata, a lokacin da aka dauke daliban daga matsugunin da suke a kauyen Gandu, lamarin da ya sa ‘yan uwansu suka yi ta zanga-zanga nan take, inda masu zanga-zangar suka bukaci a sako ƴan’uwan nasu tare da yin kira da a kara tsaurara matakan tsaro a yankin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *