January 24, 2025

Ƴan Shi’a na gudanar da zanga-zanga a Kaduna

0
image_editor_output_image1626010586-1712321660059.jpg

Daga Abdullahi I. Adam

A safiyar Juma’an nan, an ga mabiya Shi’a a tituna cikin garin Kaduna suna zanga-zanga.

Masu zanga-zangar na tafiya ne ɗauke da makamai irinsu adduna da takubba da sanduna ba kamar yadda aka saba ganin zanga-zangar lumana ba.

A yayin haɗa wannan rahoto, masu zanga-zangar sun mamaye titin Ahmadu Bello da ke tsakiyar birnin na Kaduna.

Su dai mabiya Shi’a sun sha samun arangama tsakaninsu da hukumomi musamman a garin Zaria inda an sha rasa rayuka saboda irin wannan zanga-zangar da suke gabatarwa.

Ku saurare mu domin samun ƙarin bayani.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *