December 7, 2025

Ƙazamin faɗa tsakanin ƙungiyoyin ƴan bindiga ya yi ajalin jiga-jigan ƴan ta’adda a Zamfara

images-1-27.jpeg

Abdulrazak Namadi Liman

Shuwagabannin ‘yan fashin daji guda biyu, Sani Dangote da kuma Lamo Saude, sun mutu a rikicin da ya ɓarke a Dajin Dumburun ƙarkashin karamar hukumar mulkin Zurmi ta Zamfara.

Wani rahoton jaridar Zagazola Makama ya ruwaito cewa, akalla shugabannin ‘yan bindiga biyu Sani Dangote da Lamo Saude tare da wasu mayaka 38 ne aka kashe a wani kazamin rikici da ya barke a jihar Zamfara.

Rikicin ya faru ne a ranar Lahadi 7 ga Afrilu, 2024 a ƙauyen Dumburum na ƙaramar hukumar Zurmi.

Wata majiyar leken asiri ta shaida wa Zagazola Makama cewa rikicin ya fara ne da yammacin ranar lokacin da Sani Dangote da Lamo Saude suka sake kai hari a sansanin Gwaska Dankarami.

An ce rikicin ya samo asali ne tun bayan kashe ƙanen Dangote da aka fi sani da “Mallam” da Dankarami ya yi.

Sannan an tattaro cewa Dankarami ya aike wa Dangote takardar gayyata inda ya bukaci a sasanta bai san cewa Dangote na da shirin kai masa hari ba.

A wannan kazamin faɗan bindiga da aka yi, Dankarami ya ci ƙarfin sauran ƙungiyar tare da aika su can gaba da duniya.

Ya kuma ƙwace makamansu da babura yayin da sauran mayaƙan suka gudu domin tsira da rayuwarsu.

9 thoughts on “Ƙazamin faɗa tsakanin ƙungiyoyin ƴan bindiga ya yi ajalin jiga-jigan ƴan ta’adda a Zamfara

Comments are closed.